Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsohowar Ministar Jinkai Sadiya Umar Farouk Ta Kai Kanta ofishin EFCC


Tsohuwar Ministar Jinkai, Sadiya Umar Farouk
Tsohuwar Ministar Jinkai, Sadiya Umar Farouk

Tsohuwar ministar dai tun makon da ya gabata ne ya kamata ta bayyana a ofishin na EFCC, amma dai bisa rahoton da jaridun cikin gida na Najeriya sun bayyana cewa tsohuwar ministar bata sami zuwa ba.

Tsohuwar Ministar Ayyukan Jin Kai ta Nijeriya Sadiya Umar Farouq ta gabatar da kanta a gaban hukumar EFCC a Abuja babban birnin Nijeriya.

Tsohuwar ministar dai tun makon da ya gabata ne ya kamata ta bayyana a ofishin na EFCC, amma dai bisa rahoton da jaridun cikin gida na Najeriyan suka bayyana, tsohuwar ministar bata sami zuwa ba.

Ana zargin wani dan kwangila na ma’aikatar a zamanin ministar da almundahanar makudan kudade sama da naira biliyan 37.

A safiyar Litinin din nan ne tsohuwar ministar ta wallafa a shafinta na X inda ta sanar da bayyanar ta ga ofishin hukumar ta EFCC.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG