Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Tsadar Rayuwa: Masu Zanga-Zanga Sun Kutsa Kai Cikin Ginin Majalisar Tarayya


Majalaisar Dattawa
Majalaisar Dattawa

A yau talata, mambobin kungiyar kwadago ta NLC suka kutsa kai cikin ginin Majalisar Tarayyar Najeriya dake Abuja a ci gaba da zanga-zangar da suke yi game tsadar rayuwa a kasar.

Masu zanga-zangar na dauke da kwalaye masu mabambantan sakonni a rubuce, sun isa harabar majalisar da misalin karfe 10 na safiya.

Sabanin yadda aka saba gani a baya, a wannan karon kofofin shiga majalisar sun kasance a bude, inda masu zanga-zangar suka shiga ba tare da fuskantar turjiya daga jami’an tsaro ba.

Shugaban kungiyar ta NLC, Joe Ajaero ya ce manufar gudanar da zanga-zanga a fadin kasar ita ce sanar da Shugaban Kasa Bola Tinubu game da halin kuncin da ‘yan Najeriya ke ciki.

A cewarsa, al’amarin bai takaita ga muradan NLC ba kawai harma da irin yunwar da ake fama da ita a Najeriya

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG