Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugabannin APC Sun Ziyarci Babangida Da Abdulsalam


Shugabannin APC da suka hada da Janar Buhari da Bola Tinubu sun tattauna cikin sirri da tsoffin shugabannin Najeriya, Janar Ibrahim Babangida da janar Abdulsalam Abubakar

Shugabannin sabuwar jam'iyyar hamayya ta APC a Najeriya sun kai ziyara ga wasu tsoffcin shugabannin kasar su biyu, janar Ibrahim Badamasi Babangida, da Janar Abdulsalami Abubakar, a Minna jihar Neja.

Wakilin Muryar Amurka, Mustapha Nasiru Batsari, yace shugabannin na APC, wadanda suka hada da janar Muhammadu Buhari, da Bola Ahmed Tinubu, da tsohon kakakin majalisar wakilan tarayya ta Najeriya, Aminu Bello Masari, sun tattauna da tsoffin shugabannin cikin sirri.

Daga bisani, janar Babangida ya bayyana farin cikinsa da wannan ziyara ta su, yana mai fadin cewa tilas bisa al'ada a yi marhabin da duk wanda yazo da wata shawara ta hanyar da za a iya warware matsalolin kasa.

Shugaban jam'iyyar ta APC na riko, Cif Bisi Akande, yace sun kai ziyarar ce domin neman hadin kan wadannan tsoffin shugabannin kasa.

Sai dai kuma, wani shugaban jam'iyyar ta APC, Faruk Adamu Aliyu, yace hukumar zaben Najeriya, INEC, tana neman taka musu burkin wannan rangadin da suke yi, inda ta aiko musu da takardar cewa abinda suke yin ya saba ma doka don tamkar yakin neman zabe ne.

jami'in yace zasu nazarci wannan takarda ta hukumar INEC idan sun koma Abuja domin su ga irin abinda doka ta ce kan wannan yunkurinsu na kafa sabuwar jam'iyyar a kan kafafunta.

Ga rahoton Mustapha Nasiru Batsari...
Shugabannin APC Sun Ziyarci Babangida Da Abdulsalam - 2:55
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:55 0:00
Shiga Kai Tsaye
Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG