Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Rundunar Sojin Najeriya Ta Musanta Mutuwar Janar Lagbaja


Laftanar Janar Lagbaja
Laftanar Janar Lagbaja

A ranar Asabar hukumomin sojin na Najeriya suka kore rahotanni da ke cewa an samu gibi a shugabancin rundunar sojin kasa suna masu cewa Janar Lagbaja ya tafi hutu ne.

Rundunar sojin Najeriya ta yi fatali da rade-radin da ake yi cewa Babban Hafsan Sojin Kasa Laftanar Janar Taoreed A. Lagbaja ya rasu.

A wani rubutu da ta yi da manyan haruffa akan wani labarin da aka wallafa a shafin X a ranar Lahadi, rundunar sojin ta Najeriya ta ce “Labarin na boge ne.”

Tushen labarin kamar yadda kafafen yada labaran Najeriya suka ruwaito daga Jackson Ude ne, wani tsohon hadimin shugaban kasa kuma mai sharhi a kafafen sada zumunta.

“Babban Hafsan Sojin Kasa, Taoreed Lagbaja ya mutu a wani asibiti a kasar waje tun kusan sa’ao’i 48 da suka wuce. Ya rasu ne sanadiyyar cutar daji da tsananinta ya kai mataki na uku.” Ude ya ce a shafin X.

Sai dai a sanarwar da rundunar sojin ta fitar a ranar Lahadi, ta ce batun babu gaskiya a ciki.

A ranar Asabar hukumomin sojin na Najeriya suka kore rahotanni da ke cewa an samu gibi a shugabancin rundunar sojin kasa suna masu cewa Janar Lagbaja ya tafi hutu ne.

Sai dai duk da musanta labarin da sojojin na Najeriya suka yi, Ude ya kara kalubalantar su.

“Idan rundunar sojin ta ce karya ne (abin da na fada), su fitar da bidiyon Janar Lagbaja na dakika daya a kwance akan gadon asibitinsa.” Ude ya ce a wani sabon sako da ya wallafa a shafin na X a ranar Lahadi.

Saurari rahoton Hassan Maina Kaina:

Rundunar Sojin Najeriya Ta Musanta Mutuwar Janar Lagbaja
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:25 0:00

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG