Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nijar Na Bukatar Taimakon Kasar Faransa


SHUGABA MUHAMMADOU ISSOUFOU
SHUGABA MUHAMMADOU ISSOUFOU

Kasar Nijar da kawayenta na yankin Sahel, na bukatar goyon bayan kasar Faransa, don shawo kan kasashen duniya wajan samar da kudaden gudanar da rundunar hadin gwiwa

Ministan harkokin wajen kasar Faransa Jean Yves Ledrian, ya kai ziyara a jamhuriyar Nijar, inda ya tattauna da hukumomin kasar akan maganar karfafa hulda dake tsakanin kasashen biyu musamman a wannan lokaci da batun tsaro da matsalar bakin haure ya dauki hankalin duniya.

Mahauwara akan matsalolin da yau ake dauka tafkar mafarin matsallar tsaro da kwararan bakin hauren dake zama karfen kafa ga duniya baki daya sh ne makasudin ziyarar Ministan harkokin wajen kasar Faransa Jean Yves Ledrian, kamar yadda Ministan harkokin wajen kasar Nijar, Alhaji Ibrahim Yakuba, ya bayyana.

Domin tantance irin kalubalen da gwamnatin Nijar, ke fuskanta na samarda ilimi, ga yaran kasar, Ministan na harkokin wajen Faransa, ya ziyarci makarantar Firamare Madina ta uku, dake cikin jerin makarantun dake baiwa dalibai karatu cikin harsunan gida hade da Faransanci dake birnin Yamai, abinda Ministan harkokin wajen Faransa ya ce yana bisa turba domin hakkan zai taimaka samarda ilimi mai inganci.

Akan maganar tsaro Nijar, da kawayenta na kungiyar kasashen da suka kafa rundunar hadin gwiwa domin yake da ta’addanci a yankin Sahel, na bukatar goyon bayan Faransa, don shawo kan kasashen duniya na samarda kudaden gudanar da rundunar ta hadin gwiwa.

A cewar Jean Yves Ledrian, faduwa taso dai dai da zama domin kasar Faransa ce ke shugabancin kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya a halin yanzu.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:43 0:00

Facebook Forum

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG