Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Nan Gaba Will Smith Zai Bukaci Kulawa Saboda Yana Tsufa – Jada Pinkett


Will, hagu, da Jada, dama (Tsohon hoto)
Will, hagu, da Jada, dama (Tsohon hoto)

A wannan makon fitacciyar jarumar ta fasa kwan cewa ita da Will sun rabu tun a shekarar 2016, amma ba su fadawa duniya ba.

Fitacciyar ‘yar wasan kwaikwayo a Amurka Jada Pinkett Smith, ta ce Will Smith zai bukaci wanda zai kula da shi a nan gaba, saboda tsufa na riskar shi.

Ta bayyana hakan ne yayin wata hira da ta yi da jaridar The Times.

A wannan makon fitacciyar jarumar ta fasa kwan cewa ita da Will sun rabu tun a shekarar 2016, amma ba su fadawa duniya ba.

Hakan na nufin ma’auratan sun kwashe shekaru bakwai suna basajan cew su ma’aurata ne.

A shekarar 1997 Will da Jada suka yi aure, suna kuma da ‘ya’ya biyu, Jaden mai shekaru 25 da Willow mai shekaru 22.

Will yana da wani da mai suna Trey a aurensa na farko.

Jada ta fada a hirar cewa rabuwar ta su an yi ta ne ba tare da shiga kotu ba, inda ta kwatanta lamarin a matsayin rabuwar aure ba tare da an sanya hannu a takardu ba.

Amma yayin hirarsu The Times, Jada ta ce mai yiwuwa nan gaba, za su sake komawa a matsayin miji da mata ko don ta kula da shi saboda ya fara tsufa.

A halin yanzu Jada mai shekaru 52 na zama ne a wani gida da ba shi da nisa da gidan Will mai shekaru 55.

Dandalin Mu Tattauna

Bidiyo

Saurari Dalilin Da Ya Sa Ummi Zeezee Ta Ce Tana So Ta Kashe Kanta A Hira Da Wakiliyar VOA Baraka Bashir
please wait

No media source currently available

0:00 0:06:39 0:00
Karin bayani akan Bidiyo

VOA CASU

VOA CASU: Saurari Bayanin Jarumar Kannywood, Nafeesa Abdullahi
please wait

No media source currently available

0:00 0:12:24 0:00
Karin bayani akan Bidiyo

VOA CASU

VOA CASU: Bikin Yini Na Auren Zawarawa A Kano
please wait

No media source currently available

0:00 0:02:27 0:00
Karin bayani akan Bidiyo
XS
SM
MD
LG