Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Najeriya Na Shirin Gwabzawa Da Uruguay


Za a yi karon batta yau asabar a yayin da shahararrun matasa 'yan tamaula na nahiyoyi biyu zasu kece raini a gasar cin kofin 'yan kasa da shekara 17 na duniya

Yau asabar ake shirin karon batta a tsakanin gwanayen tamaula na nahiyoyi biyu a ci gaba da gasar cin kofin duniya na samari 'yan kasa da shekara 17 a Hadaddiyar Daular Larabawa, inda Najeriya zata gwabza da Uruguay, ita kuma Cote D'Ivoure zata kara da Argentina.

Cote D'Ivoire da Argentina su zasu fara karawa a Sharjah da karfe 6 na maraice.

Daga cikin kasashen hudun da suke wasa a yau, Najeriya ce kawai ta taba lashe wannan kofin. Ba ma sau daya ko biyu ba, har sau uku. Amma zasu fuskanci kalubale daga 'yan wasan Uruguay, wadanda a cikin 'yan shekarun nan suka fara nuna kwazo sosai a wannan gasa.

Masana kwallon kafa da dama su na nuni da cewa irin takawar da Najeriya ta yi a wannan gasa a bana, ta sa ana ganin da gaske tana sahun gaba cikin wadanda suka fi kwadayin daukar wannan kofi.

A karshen zagaye na biyu na wannan gasa, Najeriya tana kan gaba, tare da kasar Brazil, a zaman wadanda suka fi jefa kwallaye a raga, inda Najeriyar ta zura kwallaye 18 a wasanni 4 da ta yi. A zagayen na biyu, Najeriya ta doke Iran da ci 4-1.

Sai dai ana ganin, kasar Uruguay ma ba kanwar lasa ba ce.
Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Halin da monoman shinkafa a Zabarmari na jihar Borno ke ciki bayan da mayakan Boko Haram suka kashe kinamin hamsin, da ya sa wasu kaura
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:41 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shugaba Donald Trump ya ba gwamnatinsa damar tasa keyar bakin haure daga kasar, da kai wasu kurkuku na Guantanamo Bay dake Cuba
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:03:00 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG