Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Matatar Man Fatakwal Zata Koma Bakin Aiki Cikin Watan Afrilu-Kyari


Matatar Mai
Matatar Mai

Shugaban kamfanin man fetur na Najeriya (NNPCL), Mele Kyari, ya bayyana cewar matatar mai ta Fatakwal zata koma bakin aiki a watan Afrilu mai zuwa.

WASHINGTON DC - Wata sanarwa ta ruwaito Shugaban NNPCL, yana cewar an kammala ayyukan gyare-gyare a matatar wacce ta karbi ganga dubu 450 ta danyen mai ta hanyar tunkudowa daga jerin bututun dake aiki.

Ya kuma kara da cewar, ana daf da kammala ayyukan gyare-gyare a matatun man Kaduna da Warri.

A cewar Mele Kyari, ana sa ran matatar man Kaduna ta fara aiki cikin watan Disamba me zuwa.

Hakan na zuwa ne bayan shekaru 3 da amincewa da kashe dala bilyan 1 da rabi wajen gyara matatar mai ta Fatakwal, daya daga cikin mafi girma a Najeriya.

Matatar man Fatakwal ita ce mafi tsufa a Najeriya, wacce aka gina a 1965, shekaru 9 bayan da aka gano man fetur a karkashin fadamu da dazuzzukan yankin Delta, inda kogin Naija ya koma tekun Guinea.

An gina matatun man Warri dake kusa da Fatakwal data Kaduna dake arewa maso tsakiyar Najeriya a shekarun da suka biyo baya, sa'annan aka ginawa matatar man Fatakwal sabon bangare a shekarar 1989.

Saidai a 'yan shekarun baya-bayan nan rashin aikin matatun yafi aikinsu yawa.

A wani labarin kuma, Majalisar Dattawan Najeriya tayi watsi da rahoton zargin yin almundahana a aikin yiwa matatun man kasar garanbawul da NNPCL ya gudanar.

Duk da kazancewarta kasa mafi arzikin man fetur a nahiyar Afirka, Najeriya ta dogara ne kacokan akan shigo da albarkatun man fetur daga ketare saboda gazawar nata matatun.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG