Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Matakin Jingine Zaben 'Yan Nijar Mazauna Ketera Na Shan Suka


Jami'a hukumar Zaben ta CENI a Nijar
Jami'a hukumar Zaben ta CENI a Nijar

Matakin jingine zaben ‘yan Nijer mazauna ketare da hukumar zaben kasar ta bayyana shirin dauka sanadiyyar annobar COVID-19, ya janyo ce-ce-ku-ce da suka daga wadanda ke wakiltar ‘yan Nijer mazauna ketare a majalisar dokokin kasa.

Wakilan sun ce ba za su yarda da dukkan wani yunkurin hana masu morar ‘yancinsu na ‘yan kasa ba.

Shugaban hukumar zabe Me Issaka Souna da yake bayani a wani taron ‘yan siyasa dangane da inda aka kwana game da tsare-tsaren zaben da ake saran gudanarwa a karshen shekarar 2020, ya ce, annobar coronavirus da ake fama da ita ba za ta bari ‘yan Nijer mazauna kasashen waje su yi zabe ba a wannan karon,.

Sai dai ra’ayoyi sun sha bamban a tsakanin ‘yan majalisar na "Diaspora" domin a ra’ayin Hon. Alfari Abbas hujjar da hukumar zabe ta CENI ta bayar wajen daukan wannan mataki bai kai matsayin da za a yi mata uzuri ba.

Kundin tsarin mulkin Nijer ya baiwa ‘yan kasar na ciki da waje matsayin guda a gaban dokar zabe, saboda haka Hon. Moumouni Issa Djibo ya ce, muddinn hukumar CENI ta yi biris da zaben ‘yan Diaspora, to za su bi hanyoyin da doka ta yi tanadi domin neman hakkinsu.

Shirya zaben cike gurbe a kasashen da annobar COIVD-19 ta hana a shirya zaben Nijer akan lokaci itace hanya mafi a’ala wajen kaucewa taka doka inji Hon. Alfari Abass.

Saurari Karin bayani cikin sauti daga Souley Moumouni Barma.

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:40 0:00

Facebook Forum

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Halin da monoman shinkafa a Zabarmari na jihar Borno ke ciki bayan da mayakan Boko Haram suka kashe kinamin hamsin, da ya sa wasu kaura
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:41 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shugaba Donald Trump ya ba gwamnatinsa damar tasa keyar bakin haure daga kasar, da kai wasu kurkuku na Guantanamo Bay dake Cuba
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 3:00 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG