Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Masu Zanga-Zangar Adawa Da Rwanda Sun Kona Tutocin Kasashen Yamma


Congo Protests
Congo Protests

Kamfanin dillancin labaran Faransa AFP ya ce masu zanga-zangar suna zargin kasashen ne da goyon bayan Rwanda ta wajen amfani da 'yan tawayen M23.

Wasu masu zanga-zangar adawa da Rwanda sun kona tutocin kasashen yamma jiya Litinin a birnin Goma da ke gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango.

Wasu masu zanga-zangar da dama, sun lullube kansu da tutar DRC, suna tattake tutocin Amurka, na Tarayyar Turai, na Faransa da kuma na Poland.

Suna kuma ɗauke da kwalayen da aka rubuta: "Ku dakatar da kisan kiyashi a DRC," "Faransa = M23/Rwanda," da kuma "Duk wanda ya yi shiru shi ma da hannunsa."

Wani mai fafutuka ya shaida wa AFP cewa, "Kasar Rwanda na kashe mu a kowace rana, kuma kasashen duniya suna goyon bayanta, shi ya sa muka kona wadannan tutoci," in ji shi.

Masu zanga-zangar, wadanda galibinsu matasa ne, sun yi tattaki ne daga tsakiyar birnin zuwa hanyar zuwa Sake kafin suka koma. Majalisar birnin Goma dai ta haramta gudanar da zanga-zangar, amma an gudanar da zanga-zangar cikin lumana, ba tare da wata arangama tsakanin 'yan sanda da sojoji ba.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG