Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Majalisar Tsaro Ta Najeriya Ta Karyata Zargin Tura Jami'an Tsaro Zuwa Masarautar Kano


Mai Baiwa Shugaban Najeriya Shawara Kan Lamarin Tsaro, Nuhu Ribadu
Mai Baiwa Shugaban Najeriya Shawara Kan Lamarin Tsaro, Nuhu Ribadu

Ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin tsaro NSA, Malam Nuhu Ribadu ya musunta zargin tura jami’ai zuwa masarautar Kano.

Tun a safiyar yau ne sarki Sunusi Lamido ya samu rakiyar mataimakin gwamna da tawagar gwamnati zuwa masarautar Kano, bayan karbar takardar maida shi aiki a jiya Juma’a.

Sabon sarki Sunusi Lamido ya zauna a fada bayan da hakimai da masoya suka kawo masa mubaya’a.

A hannu guda kuma a safiyar yau din ne Sarki mai barin gado Aminu Ado Bayero ya iso filin jirgin saman Kano da jami’an tsaro ya kuma zarce gidan sarki na Nassarawa.

A wata ganawa da manema labarai mataimakin gwamna Injiniya Abdulsalam ya ce abubuwan mamaki na faruwa a safiyar yau kawo yanzu, inda ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara na musumman a harkokin tsaro suka rako tsohon sarki Kano.

Ya ce abune da ba’a taba yinsa ba a tarihin Kano, kuma hakan ka iya haifar da fitina da tada zaune tsaye.

A gidan Nassarawa kuwa shima sarki mai barin gado ya ce suna bin umarnin kotu ne kuma babu wanda ya fi karfin hukuma.

A halin da ake ciki dai tuni gwamnan Kano da mai martaba sarki Sunusi da manyan jami'an tsaro suka shiga wata tattauna ta sirri.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG