Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ma’aikatan Lafiya Na Zimbabwe Na Iya Fuskantar Dauri Ko Tara Saboda Yajin Aiki


Yajin Aikin Ma'aikatan Lafiya a Zimbabwe
Yajin Aikin Ma'aikatan Lafiya a Zimbabwe

A ranar Talata ne kasar Zimbabwe ta rattaba hannu kan wata doka da ta haramta zanga-zanga da ma’aikatan kiwon lafiya ke shiryawa, wanda a yanzu za su iya fuskantar tara ko dauri a gidan yari na tsawon watanni shida.

Sa hannun da shugaban kasar Emerson Mnangagwa ya yi, ya zo ne bayan da ma’aikatan lafiya suka yi ta gwabza kazamin fada da gwamnati kan rashin albashi mai tsoka a shekarar da ta gabata.

Dubban ma’aikatan jinya da likitoci a asibitocin gwamnati a kasar da ke kudancin Afirka suka shiga yaji aiki a bara suna neman a yi musu karin albashi kana a biya su kudin yini ciki dalar Amurka sakamakon karyewar darajar kudin kasar da hauhawar farashin kayayyaki da ke mummunan tasiri ga albashin su.

Yaji Aikin Likitoci a Zimbabwe kan karancin kayan aiki da rashin albashi mai kyau
Yaji Aikin Likitoci a Zimbabwe kan karancin kayan aiki da rashin albashi mai kyau

Ficewar likitoci da ma’aikatan jinya ya sa asibitocin Zimbabwe ba su da isassun ma’aikata, yayin da ma’aikatan lafiya sama da dubu 4,000 suka bar kasar tun daga shekarar 2021, in ji hukumar Kula da Lafiya ta kasar a watan Nuwamban bara.

Yawancin ma’aikatan jinya a Zimbabwe suna samun kasa da dalar Amurka 100 a wata.

Reuters

XS
SM
MD
LG