Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Lukaku Ya Bar Chelsea, Ya Koma Napoli


Romelu Lukaku, dama da Antonio Conte, hagu
Romelu Lukaku, dama da Antonio Conte, hagu

Kafofin yada labaran Italiya sun ce Lukaku ya saka hannu kan kwantiragin shekaru uku a kungiyar ta Napoli wacce ke taka leda a gasar Seria A.

Dan wasan gaban Chelsea Romelu Lukaku ya isa birnin Naples na kasar Italiya inda zai kammala kaurarsa zuwa kungiyar Napoli.

Masu lura da al’amura kwallon kafa sun ce zuwan Lukaku kungiyar zai kara mata tagomashi.

Sama da magoya bayan kungiyar ta Napoli 100 ne suka tarbi Lukaku wanda dan asalin kasar Belgium ne a lokacin da ya isa don kammala binciken lafiyarsa.

Wani masoyin kungiyar ya fadi har kasa a turmutsitsin da aka yi, kuma nan take Lukaku ya tsaya ya duka don ya taimake shi kamar yadda AP ya ruwaito.

Kafofin yada labaran Italiya sun ce Lukaku zai saka hannu kan kwantiragin shekaru uku a kungiyar ta Napoli wacce ke taka leda a gasar Seria A.

Akan kudi dala miliyan 33 aka sayo dan wasan daga Chelsea in ji AP.

Dandalin Mu Tattauna

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG