Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Zai Gana Kan Rikicin Lebanon


Israel Palestinians UN Security Council
Israel Palestinians UN Security Council

Taron dimbin shugabannin kasashen duniya, wanda ya kasance kololuwar gangamin diflomasiya, na zuwa ne a daidai lokacin da hukumomin Lebanon ke cewa hare-haren isra’ila sun hallaka mutane 558, 50 daga cikinsu yara kanana.

Kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya zai gudanar da wani taron gaggawa akan kazancewar rikici a Lebanon, a cewar jakadan Slovenia a majalisar, kasar dake rike da shugabancin karba-karba na kwamitin.

Tunda fari a jiya Talata, babban sakataren Majalisar Dinkin Duniyar ya gargadi shugabannin duniya da cewar Lebanon na daf da afkawa cikin yakin yayin da hare-hare ke kara kazancewa tsakanin Isra’ila da kungiyar Hizbullahi gabanin shugaban Amurka ya gabatar da jawabinsa na bankwana a babban taron majalisar dake gudana a duk shekara.

Taron dimbin shugabannin kasashen duniya, wanda ya kasance kololuwar gangamin diflomasiya, na zuwa ne a daidai lokacin da hukumomin Lebanon ke cewa hare-haren isra’ila sun hallaka mutane 558, 50 daga cikinsu yara kanana.

Yayin da shugabannin duniya suka hallara a Manhattan domin gabatar da jawabai da ganawar diflomasiya ta gani ga ka, mamba a kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya Faransa ta bukaci a gudanar da taron gaggawa a Litinin data gabata akan wutar rikicin dake kokarin mamaye yankin gabas ta Tsakiya.

A yayin da adadin mutanen da hallaka a Lebanon ke karuwa, hankula sun kauce daga kan abinda ke faruwa a Gaza, inda babban jami’i a tarayyar turai Josep Borrell yayi gargadin cewar “muna daf da fadawa cikin yaki tsundum.”

Amurka, ta sake yin jan kunne akan kaddamar da yaki ta kasa a Lebanon, inda wani babban jami’in Amurka ya sha alwashin samarda da dabarun da majalisar zata yi amfani dasu wajen magacnce kazancewar al\amura a makon da muke ciki.

Babu tabbas game da cigaban da za’a samu wajen sassauta wutar rikici a lebanon alhli duk kokarin da ake yi na tsagaita wuta a zirrin gaza, wanda isra’ila ke cigaba da kaiwa hare-hare babu kakkautawa tun wata oktoban bara, ya ci tura.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG