Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

JOHESU Ta Ayyana Yajin Aikin Gargadi Na Kwanaki 7


Gamayyar kungiyoyin ma’aikatan jinya na Najeriya (JOHESU) ta ayyana shiga yajin aikin gargadi na kwanaki 7, tun daga tsakad daren yau Juma’a.

Yajin aikin baya-bayan nan na zuwa ne bayan cikar wa’adin kwanaki 15 da kungiyar ta baiwa gwamnatin Najeriya.

Yayin zantawarsa da manema labarai a Abuja, shugaban JOHESU na kasa, Kabiru Minjibir, ya zayyana wasu daga cikin bukatun nasu.

Bukatun sun hada da gaggauta aiwatar da dunkulallen tsarin albashin ma’aikatan jinya da biyan karin kaso 25 cikin 100 na basussukan da suke bin gwamnatin daga watan Yuni zuwa Disambar 2023 da kara shekarun ritayar ma’aikatan jinya da kuma yafe haraji a kan kudaden alawus din ma’aikatan jinya da kuma gaggauta biyan bashin alawus din shiga hatsari na lokacin annobar korona.

Kungiyar ta bukaci dukkanin mambobinta dake fadin Najeriya su yi biyayya ga wannan umarni.

Dandalin Mu Tattauna

TASKAR VOA: Yadda Tsofaffi Ke Fama Da Lalular Yanar Ido A Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Fim Da Aka Shirya Kan Leah Sharibu Ya Samu Lambar Yabo
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

TASKAR VOA: Kalubalen Da Masu Fama Da Lalurar Galhanga Ke Fuskanta
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Tasirin Cibiyar Kula Da Lafiyar Mata Da Yara Ta HopeXchange A Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:41 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG