Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hukumar N-Power Za Ta Shirya Biyan 'YAN BATCH C' Wadanda A Ke Bin Bashin Alawus


N-Power
N-Power

Ma'aikatar Jinkai da Rage radaddin talauci ta ce ta samu wasu makudan kudade a binciken da ta ke gudanarwa, saboda haka ta shirya biyan 'YAN BATCH C' wadanda ke bin bashin alawus din su har na tsawon wattani 9.

Amma kwararru a fanin zamantakewan dan Adam na cewa dole a hukunta wadanda suka yi laifi a harkar gudanar da tsarin baki daya.

Wannan mataki yana zuwa ne jim kadan bayan da Ministar Kula da Ma'aikatar Jinkai da Rage Radaddin Talauci, Betta Edu ta dakatar da shirn N-Power domin a yi bincike yawancin wadanda aka dauka aikin kula da biyan masu cin gajiyar tallafin N-Power wadanda aka fi sani da consultants.

Kafin a kai ga dakatar da shirin, mai magana da yawun hukumar N-Power Jamaludeen Kabir ya ce Kungiyar Batch 'C' ta rubuta wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu takarda cewa ba a biya su alawus din su na wattani 9 ba.

Jamaludeen ya kara da cewa binciken da Ma'akatar Jinkai ta baiyanar da inda wadannan kudade suke kuma ba da jimawa ba za a fara biyan wadanda suka ci gajiyar shirin kudaden su na wattani 9. Jamaludeen ya ce ba a riga an kammala bincike kan consultants din ba, amma an gano wadanda suka yi horo don inganta rayuwar su, kuma su ne za a biya su bashin da suke bin wannan ma'aikata.

To sai dai ga kwararre a fanin zamantakewan dan Adam kuma malami a Jami'ar Abuja, Dokta Abu Hamisu yana ganin akwai abin dubawa a wannan tsarin.

Abu ya ce kamata yayi a bi diddigi na wadanda suka yi kuskure wajen aiwatar da aikin a hukunta su, domin haka ake samun cigaba a irin wannan yanayi. Abu ya ce duk kasashen da suka cigaba sai sun bi tsari sosai sannan ake samun nasara. Ya kuma ce inza a bi shawarar sa, a bar wannan tsarin yadda ya ke amma a tabbatar da an sa ido sosai domin cire baragurbi wadanda ba sa son cigaban tsarin, kuma a hukunta su domin ya zama izina ga wasu.

Yaya, daya cikin wadanda suka ci gajiyar shirin N-Power, Mohammed Aliyu ya ji da wannan labari da ke cewa za a biya su kudaden da suke bin Ma'aikatar bashi har na wattani 9, sai ya ce, a hakikanin gaskiya yau yana cike da farin ciki, na jin wannan labari da dumidumin sa cewa za a biya su kudaden su. Aliyu ya ce yana jinjina ga Gwamnatin Tarraiya da ita Ministar Ma'aikatar Jinkai da Rage RadaddinTalauci.

Saurari rahoton:

please wait

No media source currently available

0:00 0:02:52 0:00

Dandalin Mu Tattauna

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Halin da monoman shinkafa a Zabarmari na jihar Borno ke ciki bayan da mayakan Boko Haram suka kashe kinamin hamsin, da ya sa wasu kaura
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:41 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Shugaba Donald Trump ya ba gwamnatinsa damar tasa keyar bakin haure daga kasar, da kai wasu kurkuku na Guantanamo Bay dake Cuba
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:03:00 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG