Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Harbe-Harbe da Fashe-Fashen Bama Bamai a Maiduguri Jihar Borno


Mutane suna gudu yayin da hayaki ke shiga cikin samaniya bayan da bom ya fashe a inda sojoji ke girke a garin Maiduguri. (File Photo)
Mutane suna gudu yayin da hayaki ke shiga cikin samaniya bayan da bom ya fashe a inda sojoji ke girke a garin Maiduguri. (File Photo)

'Yan Biko Haram sun kai farnaki kan sassa da dama na garin maiduguri da safiuyar yau din nan.

Rahotannin dajke fitowa daga Maiduguri na cewa ana gwabza kazamin fada a tsakanin dakarun gwamnati da 'yan Boko Haram wadanda suka far ma garin da safiyar yau Jumma'a.

Rahotanni na fadin cewa mayakan na Boko Haram sun kai farmaki kan barikin sojoji na Giwa, inda suka yi ta jefa bama-bamai, yayin da sojojin dake wurin suka maida martani da manyan bindigogi.

Haka kuma, an ce tsageran sun kai farmaki kan unguwani da dama a cikin Maiduguri inda suke harbi kan duk wanda suka gani tare da cunna ma gidaje wuta.

please wait

No media source currently available

0:00 0:03:13 0:00
XS
SM
MD
LG