Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Hamas Ta Bayyana Shirin Ci Gaba Da Mutunta Yarjejeniyar Tsagaita Wuta


A farkon makon nan Hamas ta zargi Isra’ila da keta matsayar ta hanyar ci gaba da kai hare-haren sama a yankin na Gaza hade da hana shigar da kayayyakin agaji.

Kungiyar Hamas a yau Alhamis ta bayyana shirinta na ci gaba da mutunta matsayar tsagaita wuta da ta cimma da Isra’ila yayin da masu shiga tsakani a rikicin suke kokarin ganin an ci gaba da bin wannan yarjejeniyar.

Kakakin kungiyar Abdel-Latif Al-Qanoua, ya ce Hamas ba ta da niyyar ganin rugujewar wannan yarjejeniya kuma a shirye take ta tabbatar da cewa ita ma Isra’ila ta mutunta matsayar.

“Netanyahu ya ce zai ci gaba da kai hare-hare a yankin Gaza idan har Hamas ba ta mutunta wannan yarjejeniya ba ta sakin wasu daga cikin mutanen da take garkuwa da su a ranar Asabar.”

Abdel-Latif ya soki “kalaman Firai Minista Netanyahu da na shugaban Amurka Donald Trump, yana mai cewa furucin na iya barazana ga shiri na tsagaita wuta da aka cimma.

A farkon makon nan Hamas ta zargi Isra’ila da keta matsayar ta hanyar ci gaba da kai hare-haren sama a yankin na Gaza hade da hana shigar da kayayyakin agaji.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG