Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

China Na Shirin Barin Shugaban Kasa Ci Gaba Da Mulki Har Iyakar Rayuwarsa


 Xi Jinping shugaban China na iya ci gaba da mulki har iyakar rayuwarsa
Xi Jinping shugaban China na iya ci gaba da mulki har iyakar rayuwarsa

Mahukumtan China na shirin wani kuduri da zai bar shugaban kasa ci gaba da mulki har iyakar tsawon ransa lamarin da Fadar White House ta Amurka ta ce wannan shawarar ta rage ga mahukumtar kasar ta China amma Shugaba Trump yana goyon bayan shirin takaita wa'adin shugaban kasa a nan Amurka

Fadar White House tace shirin da China take yi na janye wa’adin mulkin shugaban kasa, wani yunkurin da zai ba shugaba Xi Jinping ikon ci gaba da mulkin kasar har iya rayuwarshi, batu ne na cikin gida da ya shafi China ita kadai.

"Ina jin wannan shawara ce da China zata yanke bisa radin kanta, yadda taga yafi dacewa da kasarta" bisa ga cewar kakakin fadar White House Sarah Huckabee Sanders yayin ganawa da manema labarai jiya.

Wa’adin mulki abu ne da Trump yake goyon baya a nan Amurka, amma wannan batu ne da China zata yankewa kanta hukumci a kai, in ji ta.

Jam’iyyar kwaminis ta kasar China ta bada shawarar cire wa’adi biyu kan mulki na shugaban kasa daga kundin tsarin mulkin kasar, bisa ga rahotannin da kafofin sadarwa suka yayata ranar Lahadi.

Wannan zai karawa shugaba Xi karfi wanda tuni ake daukarsa a matsayin shugaban kasar China mafi tasiri a cikin shekaru da dama.

Jiya Litinin shugaban Amurka Donald Trump ya yabi Xi, tare da cewa akwai kyakkyawar dangantaka tsakaninsu, kuma yana matukar ganin kimar shugaban na China.

Facebook Forum

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG