Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Biden Da Trump Zasu Gana A Fadar White House


A yau Laraba Joe Biden zai gana da zababben shugaban kasa Donald Trump a fadar White House bayan da shugaban na Amurka ya sha alwashin mika mulki cikin lumana ga dan jam’iyyar Republican din daya kayar a zabe shekaru 4 da suka gabata.

Trump-wanda har yanzu bai amince da shan kaye a 2020 ba-ya samu nasarar komawa kan karagar mulkin Amurka a zaben daya gudana ranar 5 ga watan Nuwamban da muke ciki.

Biden ya shigo sahun tsirarun shugabannin Amurka da suka mika mulki ga mutanen da suka rigasu shiga fadar White House-inda hakan ta taba faruwa sa’ilin da shugaba Benjamin Harrison ya mika mulki ga Grover Cleveland a karni na 19.

Dan jam’iyyar Democrat din zai gana da Trump a ofishin shugaban Amurka (Oval Office) da misalin karfe 11 na safe agogon kasar (karfe 4 agogon GMT), kamar yadda fadar White House ta bayyana a Asabar din da ta gabata, inda lokaci ke kara karatowa na komawar tsohon shugaban kasar kan karagar mulki a watan Janairu mai zuwa.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG