Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Arangama Tsakanin Bata-Gari A Wata Kasuwa Tare Da Kone Shaguna Ya Janyo Kama Mutane 50 A Legas


'Yan sanda Najeriya yayin wani atisaye da suka yi a Abuja (Hoto: Facebook/Rundunar 'Yan sandan Najeriya - Wannan tsohon hoto ne)
'Yan sanda Najeriya yayin wani atisaye da suka yi a Abuja (Hoto: Facebook/Rundunar 'Yan sandan Najeriya - Wannan tsohon hoto ne)

A yau Alhamis, jami’an Rundunar ‘Yan Sandan Legas, suka kama wasu mutane 50 dangane da arangamar wasu bata-gari a shahararriyar kasuwar kayan abincin nan ta Ile-Epo dake karamar hukumar Alimosho ta jihar.

Hatsaniyar da ta samo asali a daren jiya Laraba ta cigaba har zuwa wayewar garin Alhamis a yayin da bangarorin bata-garin 2 ke kokarin daukar fansa game da wani al’amari da ba’a bayyana ba.

A yayin hatsaniyar ne bata-garin suka cinnawa wasu shaguna makare da kayan abinci wuta.

Tuni dai aka tura ayarin farko na masu kai dauki da suka hada da jami’an ‘yan sanda dana kwana-kwana zuwa wajen da al’amarin ya faru.

Sai dai a cikin wata sanarwa, Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Legas, Benjamin Hundeyin, yace zaman lafiya ya dawo a kasuwar.

Yace “An kama fiye da mutane 50 da ake zargi da hannu a lamarin sannan an lalata gidajen wucin gadin da suke zaune a ciki, don haka an tarwatsa su yadda ya dace”.

“Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Legas, Adegoke Fayoade, ya bada umarnin gaggauta gurfanar da bata-garin gaban kotu, sannan yayi gargadin cewar rundunar za ta sanya kafar wando daya da duk wanda aka samu yana kokarin tada zaune tsaye, kamar yadda doka ta tanadar”, a cewarsa.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG