Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Zabi Troost-Ekong Da Lookman Domin Lashe Kyautar CAF Ta Bana


Lookman, hagu, da Ekong, dama
Lookman, hagu, da Ekong, dama

Bikin mika kyautar ta CAF zai gudana ne a birnin Marrakech na kasar Morocco, a ranar 16 ga watan Disamba mai zuwa.

An zabi jagoran tawagar Super Eagles, Williams Troost Ekong da dan wasan gabanta Ademola Lookman domin fafatawa a gasar lashe kyautar hukumar kwallon kafar afrika (CAF) ta bana, a ajin maza.

Zabin Lookman baya rasa nasaba da rawar daya taka a gasar cin kofin nahiyar Afrika ta bara, inda ya zura kwallaye 3 abin da ya baiwa Najeriya kaiwa wasan karshe na gasar da kuma bajintar daya nuna a wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar turai (Europa) ta bana.

Dan wasan mai shekaru 27 ya zura kwallaye 3 rigis a raga inda ya zamo dan wasa na farko a tarihi da yayi irin wannan bajinta a wasan karshe, sannan ya baiwa Atalanta damar kungiyar kwallon kafar turai ta farko da ta lashe gasar.

Troost, da aka ayyana a matsayin dan wasa mafi bajinta a gasar cin kofin nahiyar Afrika (AFCON) ta bara, ya jefa kwallaye 3 a gasar.

Bikin mika kyautar ta CAF zai gudana ne a birnin Marrakech na kasar Morocco, a ranar 16 ga watan Disamba mai zuwa.

Dandalin Mu Tattauna

Kofin Duniya ta Qatar 2022

Kofin Duniya ta Qatar 2022
please wait

No media source currently available

0:00 0:00:32 0:00
Karin bayani akan Kofin Duniya ta Qatar 2022

Ronaldo vs. Messi

Ronaldo vs. Messi
please wait
Embed

No media source currently available

0:00 0:01:24 0:00
Satumba 30, 2020

Ronaldo vs. Messi

Karin bayani akan Wasanni
XS
SM
MD
LG