Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Gudanar Da Bikin Ranar Yafiya A Jihar Filato


Gwamna Simon Lalong (Facebook/PLSG)
Gwamna Simon Lalong (Facebook/PLSG)

Ranar bakwai ga watan Fabrairun kowace shekara ne gwamnatin jihar Filato ta ayyana a matsayin ranar yafiya bisa rikice-rikicen da jihar ta fuskanta a baya.

Al’ummomin dake zaman doya da manja a wasu sassan jihar Filato, sun kara jaddada aniyarsu ta yafe wa juna da tabbatar da zaman lafiya a tsakaninsu.

Ranar bakwai ga watan Febrairun kowace shekara ne gwamnatin jihar Filato ta ayyana a matsayin ranar yafiya wa juna kan kashe-kashe da barnata dukiyoyi da a baya aka yi a jihar ta Filato wacce ka tsakiyar arewacin Najeriya.

Bikin na bana ya janyo al’ummomin jihar ne da dama daga sassa daban-daban da suka rika bayyana irin matakan da suka dauka na yafewa juna da inganata zaman lafiya.

Karamar hukumar Barikin Ladi da a shekarun baya take kan gaba wajen yankunan da ake samun tashin hankali, yanzu an samu daidaituwa kamar yadda Muhammad Adam Muhammad da Laurence Rondon suka bayyana.

“Yau dai ranar da ake gani musamman na yafiya ne, amma ko wacce rana ta zamanto cewa ranar yafiya ne”. A cewar Muhammad Adam.

“Gaskiya mun samu zaman lafiya a Barikin Ladi, muna sake godiya ga Plateau Peace Agency kuma. Zuwan su Barikin Ladi ya sanya muka kafa kungiyar Inter Faith, A wannan kungiyar muna zama ko wani wata mu tattauna matsalolin mu da suke kauyuka da yadda za mu magance su”. A cewar Laurence.

Gwaman jihar Filaton Simon Lalong ya yi alkawarin aiwatar da bukatun al’ummar.

An gudanar da bikin yafiyar a lambun yafiya dake tsakiyar birnin Jos.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG