Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Fara Fuskantar Karancin Man Fetur a Ivory Coast, An Kuma Rufe Wasu Gidajen Jaridu


Wasu 'yan gudun hijiran rikicin Ivory Coast kenan dauke da 'yan kayakinsu.
Wasu 'yan gudun hijiran rikicin Ivory Coast kenan dauke da 'yan kayakinsu.

Jama’a a Ivory Coast suna fama da rikicin siyasar kasar, inda aka fara fuskantar karancin man fetur da kuma rufe gidajen jarida takwas.

Jama’a a Ivory Coast suna fama da rikicin siyasar kasar, inda aka fara fuskantar karancin man fetur da kuma rufe gidajen jarida takwas.

Masu kamfanonin jaridun masu zaman kansu sun fito da bayanai na hadin gwiwa a yau Talata inda su ka yi nuni da yadda magoya bayan shugaban da ke kan gado Laurent Gbagbo ke ta amfani da bangaren doka da ‘yan sanda wajen gallaza masu. Kamfanonin jaridan sun ce an auna su ne saboda kawai sun ki su goyi bayan Mr. Gbagbo.

Shugaban ya yi biris da matsin lambar al’ummomin duniya na bukatar ya sauka ya kuma mika ragamar iko ga Alassane Ouattara, wanda akasarin kasashe su ka ayyana a matsayin wanda ya ci zaben shugaban kasar da aka gudanar a watan Nuwamba.

A wata sanarwa a yau Talata, kungiyar rajin kare ‘yancin ‘yan jarida mai suna Reporters Without Borders a turance ta ce ana gallazawa tare da yi wa kamfanonin jarida masu zaman kansu barazana. Kungiyar ta kuma ce an fara yakin kafafen yada labarai tsakanin magoya bayan Gbagbo da magoya bayan Ouattara, wanda hakan ya haifar da yana mara kyau ga ‘yan jarida.

Kungiyar ta ce wasu mutane dauke da kulake da adduna sun hallaka wani ma’aikacin kamfanin jaridar da ke goyon bayan Gbagbo a Kudancin Abidjan ranar Litini.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG