Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

An Aurar Da Wasu Daga Cikin ‘Yan matan Neja 100 Da Aka Dage Aurensu


Jihar Neja
Jihar Neja

Malaman addini da wani ‘dan majalisar dokokin jiha sun dakatar da shirinsu na aurar da mata da ‘yan mata 100 a yankin Arewacin Najeriya bayan da lamarin ya haifar da bacin rai.

WASHINGTON, D. C. - Sai dai wasu a cikin ‘yan matan an daura musu auren a wani biki na sirri, kamar yadda kakakin majalisar jihar Neja kuma daya daga cikin ‘yan matan suka bayyana a ranar Talata.

Shirye-shiryen daurin auren da aka yi a jihar ta Neja mai rinjayen Musulmi sun fuskanci suka daga ministar harkokin mata Uju Kennedy-Ohanenye da wata kungiyar kare hakkin a yankin da ta kaddamar da koken dakatar da bikin. Masu suka dai na fargabar cewa 'yan matan, wasu daga cikinsu marayu ne, kuma wasu sun kasa a shekarun yin aure.

Tawagar ma'aikatar harkokin mata ta ziyarci Neja a ranakun Alhamis da Juma'a inda ta gana da kakakin majalisar dokokin jihar Abdulmalik Sarkindaji da wasu limaman yankin da wasu daga cikin 'yan matan, kamar yadda kakakin Sarkindaji Auwal Mohammed ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.

Mohammed ya ce tawagar ta gamsu da cewa ‘yan matan sun haura shekaru 18, wato shekarar aurar da su bisa doka. Kuma ma’aikatar ta yi alkawarin bayar da tallafin karatu ga duk wadanda ke son ci gaba da karatunsu da kuma tallafin kudi ga masu son yin auren.

-Reuters

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG