Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Afrika Ta Kudu Na Shirin Bada Rigakafin Da Ba A Amince Da Shi Ba


Ma'aikatan lafiya a Afrika ta Kudu
Ma'aikatan lafiya a Afrika ta Kudu

Afirka ta Kudu za ta fara yiwa ma’iakatan lafiya allurar rigafi da allurar rigakafin coronavirus da ba amince da ita ba da kamfanin harhada magunguna na Johnson & Johnson a mako mai zuwa, don ganin ko tana hana kamuwa da sabon nau’in cutar da ya bulla a kasar.

Ministan Lafiyar kasar Zweli Mkhize ya fada yau Laraba cewa, Afirka ta Kudu za ta jingine shirinta na amfani da allurar rigakafin Oxford da AstraZeneca a yanzu, saboda damuwa da ta yi ko tana aiki kan sabon nau’in cutar N501Y.

Ministan lafiyar kasar ya ce masana kimiyyar kasar za su ci gaba da duba allurar rigakafin AstraZeneca da kuma bada shawara ko su yi musayar allurar rigakafin kafin lokacinta ya kare.

Kamfanin dillacin labarai na Associated Press ya rawaito Mkhize ya fada a gidan talabijin na kasar, allurar rigakafin daya ta Jonhson & Jonson tana da kyau, bisa gwaji da aka yiwa mutane dubu 44,000 a Afirka ta Kudu da Amurka da kuma Yankin Latin Amurka.

Ko da yake, har yanzu babu wata kasa da ta amince da allurar rigakafin ta Jonson & Jonson. Sai dai kamfani a makon da ya gabata ya nemi izinin yin amfni da ita na gaggawa a Amurka.

Ana sa ran Afirka ta Kudu za ta yi amfani allurar rigakafin Pfizer da wasu don taimakwa shirin rigakafin.

Afirka ta Kudu ita ce tafi kowace kasa yawan masu harbuwa da COVID-19 a Nahiyar Afirka, tare da sama da mutane 1,479,000 wadanda aka tababtar sun kamu da kuma 46,869 da suka mutu, a cewar Cibiyar Tattara bayanai ta Jami’ar Johns Hopkins.

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:03:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 0:02:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
Malam Bello Abba Yakasai masani kan harkokin noma ya yi karin haske akan matsalar tsaro ga manoma da hanyoyin magance wannan matsala
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p

No media source currently available

0:00 0:04:20 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 810p
  • 720p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG