Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Kogi Na Cikin Jihohin Dake Samar Da Danyen Mai - Ododo


Bututun mai
Bututun mai

Ya koka a kan cewa duk da gano man da tarin yawa a Kogi, jihar ba ta cin gajiyar rabon kaso 13 cikin 100 da ake baiwa jihohin dake samar da danyen mai a Najeriya.

Gwamnan Kogi, Usman Ododo, ya bayyana cewar jihar na sahun jihohin dake samar da danyen mai sakamakon samun rijiyoyinsa da dama da aka yi a karamar hukumar Olamaboro ta jihar.

Sai dai, ya koka a kan cewa duk da gano man da tarin yawa a Kogi, jihar bata cin gajiyar rabon kaso 13 cikin 100 da ake baiwa jihohin dake samar da danyen mai a Najeriya.

Gwamna Ododo ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci Ministan Albarkatun Man Fetur, Heineken Lokpobiri, a ofishinsa dake Abuja a yau Alhamis.

Ya bukaci samun goyon bayan ma’aikatar a kokarin da jihar Kogi ke yi na shiga sahun jihohin arewacin Najeriya dake neman a fara hakar mai a cikinsu.

A cewar Ododo, Kogi ce mahadar yankunan kudanci da arewacin Najeriya a aikin shimfida bututun iskar gas daya tashi daga Ajaokuta zuwa Kaduna ya zarce Kano (AKK), abin da ya bata babbar damar a harkar zuba jari a fannin mai da iskar gas.

A martaninsa, Lokpobori yace gwamnatin tarayyar Najeriya, ta hannun hukumar kula da cinikin albarkatun man fetur, na nazari a kan batun kasancewar Najeriya na bukatar karin danyen mai da iskar gas domin kara kudin shigarta, inda take harin fitar da ganga miliyan 5 a kowace rana daga ganga miliyan 2.5.

Dandalin Mu Tattauna

TASKAR VOA: Yadda Tsofaffi Ke Fama Da Lalular Yanar Ido A Nijar
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Fim Da Aka Shirya Kan Leah Sharibu Ya Samu Lambar Yabo
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

TASKAR VOA: Kalubalen Da Masu Fama Da Lalurar Galhanga Ke Fuskanta
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:26 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
TASKAR VOA: Tasirin Cibiyar Kula Da Lafiyar Mata Da Yara Ta HopeXchange A Ghana
please wait

No media source currently available

0:00 0:03:41 0:00
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG