Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

NNPCL Zai Sayar Da Litar Man Dangote Tsakanin N950 Da N1,019


Mai magana da yawun kamfanin na NNPCL, Olufemi Soneye, ne ya bayyana hakan a yau litinin cikin wata sanarwa.

Kamfanin man fetur din Najeriya (NNPCL) ya bayyana cewar zai sayar da litar fetur din daya saya daga matatar man dangote akan kudin da bai gaza Naira 950 ba a jihar legas.

A cewar sanarwar, “kamfanin mai na NNPCL ya fitar da jadawalin kiyasin farashin man fetur din da ya sayo daga matatar Dangote a ilahirin gidajen mansa dake fadin kasar.

“Kamfanin NNPCL na bada tabbacin cewar ya sayi man fetur daga matatar Dangote a watan Satumbar da muke ciki a kan farashin kudin dala, kasancewar ba za a fara ciniki da takardar kudin naira ba sai a ranar 1 ga watan Oktoba mai kamawa.”

Sanarwar ta kuma kara da cewar mafi kankantar farashin da za a sayar da litar man ba zai gaza Naira 950 a jihar Legas da kewaye.

Ta ci gaba da cewa farashin na iya kaiwa har Naira 1, 019 a jihohi irinsu Borno, kana Abuja, Sokoto, Kano, sauran jihohi kuma za a sayar da shi akan Naira 999, 22.

A yayin da jihohin Oyo da Rivers da sauran sassan kudancin Najeriya, za’a sayar da litar man a kan Naira 950.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG