Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Ci Gaba Da Kokarin Ceto Mutanen Da Zaftarewar Kasa Ta Rutsa Da Su A Kasar Habasha


Zaftarewar kasa a Habasha
Zaftarewar kasa a Habasha

An ci gaba da kokarin ceto mutane har ya zuwa yammacin jiya Talata a yankin Gofa, bayan zaftarewar kasa yayi sanadiyyar mutuwar akalla mutane 229 a kudancin kasar Habasha.

Adadin na wadanda suka mutu ya hada da mutane da dama da kasa ta binne su a ranar Litinin, a yayin da ma’aikatan ceto suka karade yankin domin ceto masu sauran rai daga wata zaftarewar kasa a ranar Lahadi, a cewar hukumomin kasar.

Ruwan sama kamar da bakin kwarya ne suka haddasa zabtarewar kasar a gunduma mai nisa ta Kencho Shacha Godzi ta kasar Habasha.

Zaftarewar kasa a Habasha
Zaftarewar kasa a Habasha

Daga cikin wadanda suka mutu har da kananan yara da mata masu juna 2, a cewar wani jami’in yankin, ya kara da cewa an sami zaro mutane akalla 5 da ran su.

Firai Minista Abiy Ahmed ya ce an tura jami’an hukumar kula da bala’o’i ta kasar zuwa yankin, domin taimakawa wajen aikin bincike da ceto.

Dandalin Mu Tattauna

Alkaluma daga watan Janairu sun nuna ana ci gaba da samun hauhawar farashin kayan abinci, na mai da na gidaje da sauransu a Amurka
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 3:02 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA

Zaben 2023

Bayan wasu shekaru kasuwanni na rufe saboda matsalar tsaro a yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, a yanzu harkoki sun fara dawowa
please wait
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p

No media source currently available

0:00 2:31 0:00
  • Auto
  • 240p
  • 360p
  • 480p
  • 720p
  • 810p
Karin bayani akan Rahotannin Taskar VOA
XS
SM
MD
LG