Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Ana Ci Gaba Da Kokarin Ceto Mutanen Da Zaftarewar Kasa Ta Rutsa Da Su A Kasar Habasha


Zaftarewar kasa a Habasha
Zaftarewar kasa a Habasha

An ci gaba da kokarin ceto mutane har ya zuwa yammacin jiya Talata a yankin Gofa, bayan zaftarewar kasa yayi sanadiyyar mutuwar akalla mutane 229 a kudancin kasar Habasha.

Adadin na wadanda suka mutu ya hada da mutane da dama da kasa ta binne su a ranar Litinin, a yayin da ma’aikatan ceto suka karade yankin domin ceto masu sauran rai daga wata zaftarewar kasa a ranar Lahadi, a cewar hukumomin kasar.

Ruwan sama kamar da bakin kwarya ne suka haddasa zabtarewar kasar a gunduma mai nisa ta Kencho Shacha Godzi ta kasar Habasha.

Zaftarewar kasa a Habasha
Zaftarewar kasa a Habasha

Daga cikin wadanda suka mutu har da kananan yara da mata masu juna 2, a cewar wani jami’in yankin, ya kara da cewa an sami zaro mutane akalla 5 da ran su.

Firai Minista Abiy Ahmed ya ce an tura jami’an hukumar kula da bala’o’i ta kasar zuwa yankin, domin taimakawa wajen aikin bincike da ceto.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG