Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Shugaba Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Komawa Tsohon Taken Najeriya


Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, a ranar Ma'aikata ta Duniya
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, a ranar Ma'aikata ta Duniya

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya tabbatar da hakan yayin zaman hadakar majalisar a yau Laraba.

Shugaba Bola Tinubu ya sanya hannu kan kudiri da hadakar majalisar dokokin Najeriya ta zartar kan komawa tsohon taken kasar ta “Nigeria, we hail thee” a turance.

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya tabbatar da hakan yayin zaman hadakar majalisar a yau Laraba.

Sanata Godswill Akpabio ya kara da cewa zaman Majalisar ta yau ta musaman ce saboda tabbatar da komawa tsohon taken na ''Nigeria, we hail thee" a turance.

Sai dai yace Shugaba Tinubu ba zai gabatar da jawabi ba kamar yadda ake zato saboda zai halarci bikin kaddamar da shirin 'Abuja Metro Line'.

Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai a lokuta daban-daban suka zartar da kudirin komawa tsohon taken Najeriya cikin mako daya.

An maye gurbin tsohon taken daya soma da "Nigeria, we hail thee" a turance da wanda ya soma da “Arise o' compatriots" a shekarar 1978.

Tsohon taken da aka kirkira lokacin da Najeriya ta samu 'yancin kai a ranar 1 ga watan Oktoban 1960 zai maye gurbin wanda ake amfani dashi a halin yanzu.

Manufar kudirin shine sake farfado da tsohon taken da aka yi watsi dashi a 1978 lokacin gwamnatin mulkin sojan Olusegun Obasanjo.

Wani bakon haure dan asalin Burtaniya daya zauna a Najeriya mai suna Jean Williams ne ya rubuta taken na "Nigeria, we hail thee " .

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG