Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

KALLABI: Hira Da Linda Umaru PT1 Da Nazari Kan Kalubalen Rayuwa A Najeriya


Alheri Grace Abdu
Alheri Grace Abdu

Shirin kallabi na wannan makon, wanda ya kasance na farko a shekara ta 2024, ya yi nazarin kalubale da aka fuskanta a Najeriya a shekarar da ta gabata tare da bada shawarwari kan yadda za a sami ingancin rayuwa a bana. Bakin da muka gayyata domin tsokaci kan wannan mukala sun hada da malamar makaranta Khadija Idris, da matar wani mai Unguwa, Jamila Hamisu Mai Iyali, da kuma uwargida uwar daki, Abida Sani.

Kallabin shirin ta mako kuma ita ce, Linda Umaru, wata 'yar asalin jihar Gombe da take da bude katamfaren shago da take sanarkitso da saida kayan kitso, tana kuma sayar da abincin gida Najeriya, da ta yi fice ainun a jihar California.

Kallabi-Linda Umaru PT1
please wait

No media source currently available

0:00 0:22:04 0:00

  • 16x9 Image

    Grace Alheri Abdu

    Grace Alheri Abdu  babbar Edita ce (Managing Editor) a Sashen Hausa na Muryar Amurka wadda ta shafe sama da shekaru 30 tana aikin jarida. Tana da digiri na biyu a fannin dokoki da huldar diplomasiyar kasa da kasa, da kuma digiri na biyu a fannin nazarin addinan al'adun gargadiya na kasashen Afrika.

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG