Yadda Wasu Matasa Suke Tsaftace Muhimman Wurare Da Ake Ba-haya A Jos

Your browser doesn’t support HTML5

Matsalar masu yin ba-haya a waje a Najeriya, matsala ce da ta jima tana ci wa hukumomi tuwo a kwarya.
Yin ba-haya a bainar jama’a matsala ce babba da ake fama da ita a wasu biranen Najeriya, lamarin da ke haifar da barkewar cututtuka kamar kwalara da typhoid. Ganin haka ne ya sa wasu matasa a Jos da ke jihar Filato suka dukufa wajen raba muhimman wurare a tsakiyar birnin da wannan matsala. Ga Iliyasu Kasimu da rahoton.