Wata Kungiya Mai Suna HED TAMAT a Junhuriyar Niger Ta Fara Yekuwar Zaman Lafiya

  • Ladan Ayawa

The President of Niger, Mahamadou Issoufou, addresses the media during a joint press conference with German Chancellor Angela Merkel, unseen, after a meeting at the chancellery in Berlin, Germany, Wednesday, May 8, 2013. (AP Photo/Michael Sohn)

Kungiyar nan da ake kira HED TAMAT a jamhuriyar Niger ta fara ran gadin ganawa da shugabanni al'umma musammam sarakuna domin samar da zaman lafiya a kasa.

Wata kungiya mai zaman kanta da ake kira Hed Tamat dake a jamhuriyar Niger ta fara zagaye domin wayarda kan al’umma kan muhimmancin samar da zaman lafiya.

Kungiyar ta fara ganawa da shugabannin al’umma musammam sarakunan gargajiya domin su taimaka su bada tasu gudunmowar wajen samar da zaman lafiya.

Daya daga cikin shugabannin kungiyar Mani Agali yace suna ganawa da shugabannin al’umma ne domin ko wani bako ko wani sabon addini da zai bulla a yankunansu sune na farko da zasu samu labarin hakan.

Ga Tamar Abari da Karin bayani

Your browser doesn’t support HTML5

Wata Kungiya Mai Suna HED TAMAT a Junhuriyar Niger Ta Fara Yekuwar Zaman Lafiya. 3'08