Turkiya Na Shirin Kawo Karshen Yaki Da ISIS

Shugaban Kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan

Kasar Turkiya za ta ayyana kawo karshen yakin watanni bakwai da take gudanarwa a arewacin kasar Syria domin fatattakar 'ya'yan kungiyar ISIS da Kurdawan Syria daga yankin dake kan iyakar kasar.

Ba’a tantance yadda aikin sojojin Turkiya zai canja cikin Syria ba inda sojojin gwamnati da mayakan sa kan kungiyar ISIS da sojojin Kurdawa da kuma wasu kungiyoyin 'yan tawaye su ke gasar mallakar yankin.

A watan Augusta aka fara wannan aiki na fatattakar 'yan kungiyar ISIS.

Gwamnatin Turkiya ta na daukar mayakan Kurdawa a zaman wani bangare da 'yan kungiyar Kudistan Workers Party ko kuma PKK a takaice wadda ta share shekaru 30 ta na tawaye a kudu maso gabashin kasar ta Turkiya.

Amurka wadda take jagorancin sojojin taron dangi wadanda suke kai wa 'yan kungiyar ISIS hare-hare da jiragen saman yaki ta na goyon bayan mayakan Kurdawa, ta na daukar su a zaman mayakan da za su iya fatattakar 'yan ISIS daga yankin.