Tsohon Firai Ministan Nijar Hama Amadou Ya Rasu

Hama Amadou

A bara ne Amadou da ke hijira a kasashen waje ya koma gida da nufin ba da gudunmowa a kokarin fitar da kasar daga dambarwar siyasar da ta biyo bayan juyin mulkin 26 ga watan Yulin 2023.

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa Tsohon Firai Ministan Jamhuriyar Nijar Hama Amadou ya rasu.

Amadou wanda har ila yau tsohon Kakaki ne a Majalisar Dokokin Nijar ya rasu ne a birnin Yamai bayan fama da rashin lafiya.

A bara ne Amadou da ke hijira a kasashen waje ya koma gida da nufin ba da gudunmowa a kokarin fitar da kasar daga dambarwar siyasar da ta biyo bayan juyin mulkin 26 ga watan Yulin 2023.

A yayin da magoya bayansa ke cewa zai taimaka a shayo kan takun sakar da ke tsakanin kasar da kungiyar ECOWAS wasu kuwa sun bukaci madugun ‘yan hamayyar ya kai kansa mashara’anta saboda laifukan da ake zargin ya aikata a baya.

Amadou ya shafe shekaru biyu a tsakanin Faransa da sauran kasashen duniya cikin wani yanayin da ke kama da gudun hijira mai nasaba da matsalolin da ya fuskanta a zamanin da shudediyar gwamnati.

A shekarar 2013 gwamnatin shugaba Issouhou Mahamodu ta zarge shi da laifin sayen jarirai daga Najeriya inda ya arce daga Nijar a watan Agustan 2014 jim kadan bayan da kwamitin jagorancin majalisar ya cire masa rigar kariya a wani shirin gurfanar da shi a gaban kotu.

Bayan dawowar shi gida a shekarar 2016 da 2020 madugun ‘yan hamayyar ya bakuncin kurkuku a washegarin zaben 2021 saboda zarginsa da yunkurin ta da zaune tsaye.

Saurari rahoton Souley Moumouni Barma:

Your browser doesn’t support HTML5

Tsohon Firai Ministan Nijar Hama Amadou Ya Rasu