Sudan ta Kudu: Jakada Ya Ja Hankalin Amurka Kan Shirin Janye Tallafi

Shugaban Sudan ta Kudu Salva Kiir

Jakadan kasar Sudan ta Kudu a Amurka, Gordon Buay, ya yi kira ga gwamnatin Amurka da ta sake tunani kan janye taimakon da take ba kasarsa saboda acewarsa, yin hakan zai shafi shirin zaman lafiya a kasarsa.

Wani babban jami’in diplomasiyar Sudan ta Kudu a Amurka ya yi kira ga Amurka da ta sake tunani kan shirin janye taimako da take bai wa Sudan ta Kudu.

A cewar Gordon Buay, hakan wani koma baya ne ga shirin samun zaman lafiyar kasar.

Jakada Buay, babban jakadan Sudan ta Kudu a Washington, ya fada cewa sanarwar da fadar White House ta fitar a shekaranjiya Talata da kakkausar kalamai a kan Sudan ta Kudu ka iya yin mummunar tasiri.


Ya kara da cewa wannan mataki zai aike da sakon da zai haifar da rashin fahimta ga 'yan tawayen kasar.