Me Ya Sa Kasashen Burkina Faso Da Mali Ke Kokarin Komawa ga Rasha a Maimakon Faransa (ii)

  • Ibrahim Garba

Ibrahim K Garba

Yau za a ji karshen amsar wannan muhimmiyar tambaya kan dalilan wasu kasashe rainon Faransa na canza sheka.

Masu sauraronmu assalamu alaikum barkanmu da sake saduwa a wannan shirin na amsoshin tambayoyinku, Da fatan masu azumi an sha ruwa lafiya.

Yau za a ji kashi na biyu kuma na karshe na maimaicin amsar tambayar nan kan dalilan kasashen Mali da Burkina Faso na shirin kulla yarjejeniya da kasar Rasha, da kaurace ma kasar Faranasa; da kuma yadda al’amarin zai kasance?

Masu tambayar, idan an tuna, su ne: Babandi Mamman Bande,
da Tasiu Unguwar Tudu, Damagaram da Issuhu Madatai, da Ali Sarkin yakin Ni'ma, da Shugaba Iliya Maishayi Garkin Daura.

Ga karashin amsar da wakilin Muryar Amurka a Kano, Mahmud Ibrahim Kwari, ya samo daga wurin furfesa Kamilu Sani Fagge na Jami’ar Bayero da ke Kano.

A sha bayani lafiya:

Your browser doesn’t support HTML5

04-22-23-AMSOSHIN TAMBAYOYINKU.mp3