Lauyoyi Mata Sun Jajirce Don Yakar Cin Zarafin Mata Da Yara a Najeriya

Taron Kungiyar Mata Lauyoyi a Jos

Kungiyar mata lauyoyi reshen jahar Pilato ta ce za ta jajirce don ganin an kawo karshen cin zarafin mata da yara a Najeriya.

A wani taron kara wa juna sani na mako guda da kungiyar mata lauyoyin suka shirya a Jos, shugaban kungiyar Mary Izam ta ce yawan rahotannin cin zarafi da suka samu lokacin dokar hana yawo saboda cutar Coronavirus a Jahar Pilato ya sa su damarar yaki da mugayen dabi’un.

Malam Nurudden Usaini Magaji, wanda ya gabatar da jawabi a wurin taron bitar, ya ce dole sai dukkan masu ruwa da tsaki sun hada hannu don shawo kan wannan lamarin.

Tsohuwar kwamishinan ma’aikatar mata da walwalar jama’a a jahar Pilato, Barista Olivia Dazyem, cewa ta yi kamata yayi a yi garambawul wa dokokin da suka shafi cin zarafin mata da yara.

Domin karin bayani saurari rahotan Zainab Babaji.

Your browser doesn’t support HTML5

Lauyoyi Mata Sun Jajirce Don Yakar Cin Zarafin Mata Da Yara a Najeriya 3'09"