Karin Mutane 23 Sun Kamu Da Coronavirus a Kano

A karon farko ba a samu sabbin alkaluman wanda suka kamu da cutar coronavirus ba a jihar Legas.

Amma jihar Kano ta samu karin sabbin mutane 23 da suka kamu da cutar coronavirus, a yanzu haka jimlar wadanda suka kamu a jihar ta kai 59.

A jihar Gombe an samu karin mutum biyar, uku a Kaduna, biyu a jihohin Borno da Abia, sai kuma jihohin Sokoto, Ekiti da Abuja da aka samu daya-daya.

Rahoton da cibiyar kula da dakile cututtuka masu yaduwa ta NCDC ta fitar ya nuna cewa adadin masu dauke da cutar coronavirus a Najeriya yanzu ya kai 665, sannan mutane 188 sun samu lafiya a fadin kasar, yayin da mutane 22 suka mutu.

Saurari karin bayani cikin sauti daga Babangida Jibrin.

Your browser doesn’t support HTML5

Karin Mutane 23 Sun Kamu Da Corona Virus a Kano