Jihohi Bakwai, Birnin Tarayya Na Fama Da Matsalar Katsewar Wutar Lantarki A Najeriya

Masu gyaran wutar lantarki.

A karo na biyu cikin watanni biyu da rabi , an samu rugujewar cibiyar wutar lantarki ta kasa a Najeriya, lamarin da ya jefa jihohi bakwai da babban Birnin Tarayya Abuja cikin duhu.

Wannan matsala ta jawo kiraye-kiraye ga gwamnatin tarayya da ta sake duba harkar sayar da hannun jarin wutar lantarki da aka yi a kasar.

Jihohin da abin ya shafa sun hada da Legas, Enugu, Kaduna, Abia, Anambra, Ebonyi, Imo da kuma Birnin Tarayya Abuja.

Tabbacin rugujewar cibiyar wuta ta kasa ya bayyana ne a wata takarda mai dauke da sa hannun kampanin wuta ta Legas ga dukan wadanda ke sayan wuta ta hannunsu, cewa an samu matsala a cibiyar wutar lantarki ta kasa kuma ta shafi wadannan Jihohin.

Shugaban Kungiyar Kare Hakkin Masu Amfani da wutar lantarki a Najeriya wato Consumer Protection Network Initiative a turanci, Kola Olubiyo ya ce wannan hali na rashin wuta ya sa kungiyarsa ta aike wa shugaba Muhammadu Buhari takarda ta musamman.

Amma mai ba Shugaban Kasa Shawara a harkar Manyan ayyuka, Ahmed Zakari, ya ce gwamnati tana aiki tukuru wajen magance matsalar.

Abin jira a gani shi ne irin matakin da mahukunta za su dauka domin biya wa masu amfani da wutar latarki bukatunsu na yau da kullum.

Saurari cikakken rahoton cikin sauti:

Your browser doesn’t support HTML5

Jihohi 7 Da Birnin Taraiyya Suna Fama Da Rashin Wuta A Najeriya