INEC Ta Dage Zaben Najeriya

INEC

Hukumar Zaben Najeirya INEC, ta dage zaben shugaban kasar da za a yi a yau Asabar zuwa 23 ga watan Fabrairu.

A wani taron manema labarai da hukumar ta gudanar dazun nan da misalin karfe 2 na dare agogon Najeriya, Shugaban hukumar Prof. Yakubu Mahmood, ya ce bayan lura da wasu batutuwa da suka shafi shirye-shiryen zaben, hukumar ta lura da cewa, gudanar da zaben ba zai yiwu ba.

“Wannan mataki da hukumar ta dauka bai zo mata da dadi ba, amma ya zama dole a dauke shi, domin zai taimaka wajen samar da sahihin zabe.” Inji Prof. Mahmood.

Ya kara da cewa, “hukumar za ta zauna da masu ruwa da tsaki domin ta fada masu halin da ake ciki a yau da misalin karfe 2 na rana (agogon Najeriya).”

A da, an tsara za a yi zaben na Najeriya a yau Asabar bayan da aka kammala yakin neman zabe a ranar Alhamis.

Your browser doesn’t support HTML5

INEC Ta Dage Zaben Najeriya