Ina Aka Fi Tsawon Sa'o'in Azumi, Ina Kuma Aka Fi Gajartar Sa'o'in Azumi?

  • Ibrahim Garba

Ibrahim K Garba

Baya ga amsar tambaya kan inda aka fi tsawon sa'o'in azumi da kuma inda aka fi gajartar lokacin, akwai kuma maimaicin amsar tambaya kan dalilan kasashen Mali da Burkina Faso na karkata daga Faransa zuwa ga Rasha

Masu sauraronmu assalamu alaikum barkanmu da sake saduwa a wannan shirin na amsoshin tambayoyinku, Da fatan masu azumi kuma ana kan ayyukan ibada lafiya.

TAMBAYA 1: Don Allah, a tambaya mana masana:- Wace kasa ce, ko kuma al'umma, ke yin mafi tsawon sa'o'in azumi, ko mafi gajartar sa’o’in azumi, a duniya?

MASU TAMBAYAR: Zakaria Salifu Gidan Rumji da Adamu Shamuwa mai Dawaki a Shikal Jamhuriyar Nijar.

TAMBAYA 2: Za kuma a ji maimaicin tambayar nan kan dalilan kasashen Mali da Burkina Faso na shirin kulla yarjejeniya da kasar RASHA, da kaurace ma kasar Faranasa; da kuma yadda al’amarin zai kasance?

MASU TAMBAYAR (Idan an tuna, su ne): Babandi Mamman Bande,
da Tasiu Unguwar Tudu, Damagaram da Issuhu Madatai, da Ali Sarkin yakin Ni'ma, da Shugaba Iliya Maishayi Garkin Daura.

AMSOSHI:

Ga amsar tambaya ta daya daga bakin Dr. Adamu Baɓikkoi, malami a Kwalejin Horas da Malamai ta Gwamnatin Tarayya dake Yola, jihar Adamawa, Najeriya.

Tambaya ta biyu kuma, dama Farfesa Prof Kamilu Fagge na Jami’ar Bayero ta Kano ne ya amsa ta.

A sha bayani lafiya:

Your browser doesn’t support HTML5

04-15-23 AMSOSHIN TAMBAYOYINKU.mp3