Gwamnatin Nason Daukar Matakai Domin Fatattakar ‘yan Boko Haram Daga Yankin

Kimanin ‘yan gudun hijira dubu goma sha biyu ne suka kwarara zuwa yankin tafkin Chadi bayan da kwanankin baya Gwamnan jihar Diffa ya bada umarnin cewa jama’ar dake yakin kuma ke da matsalar Boko haram su kauracewa yankin.

Yace kauracewa yankin ya zama wajibi domin Gwamnatin nason daukar matakai domin fatattakar ‘yan book Haram daga yankin.

Wakilin muryar Amurka Shuaibu Mani, yace akwai tsoron barkewar annobar cututtuka a wannan yankin domin yawan jama’a da ke kwarara wannan yankin.

Yakara da cewa ‘yan gudun hijiran na bukatar taimako masamman na abinci da wurin kwana koda yake wasu kungiyoyin sa kai suna taimakawa da abinci da kuma gida sauro.

Your browser doesn’t support HTML5

'Yan Gudun Hijira - 2'47"