Sa'o'i kadan bayan da hukumomi a Najeriya suka sauya alkaluman mutanen da cutar coronavirus ta kama a kasar, hukumar kare yaduwar cututtuka ta NCDC ta ce adadin ya kai 214.
Da yammacin ranar Asabar NCDC ta ce mutum 209 suka kamu da cutar ba 210 kamar yadda aka sanar a ranar Juma'a ba. https://bit.ly/2RbWfsW.
Amma sa'o'i bayan gyara wannan kuskure, hukumar ta ce adadin ya kai 214 a yau.
"Da misalin karfe 10:10 na dare ranar 4 ga watan Afrilu, mutum 214 ke dauke da cutar #COVID19 a Najeriya." Shafin NCDC na Twitter ya ce.
Five new cases of #COVID19 have been reported in Nigeria: 3 in Bauchi and 2 in the FCT.As at 10:10 pm 4th April there are 214 confirmed cases of #COVID19 reported in Nigeria. Twenty-five have been discharged with four deaths pic.twitter.com/NDz5FFMrdF
— NCDC (@NCDCgov) April 4, 2020
Adadin ya haura 209 ne bayan "an samu sabbin mutum biyar da #COVID19 a Najeria, uku a Bauchi, biyu a Abuja." NCDC ta ce.
Ya zuwa yanzu, mutum hudu sun mutu an kuma sallami 25 a Najeriya.