Buhari Ya Bukaci Wakilan Najeriya a Gasar Karatun Alkur'ani Mai Tsarki Su Zama Na Gari

Wasu yara na karatun Alkur'ani Mai Tsarki

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya shawarci wadanda za su wakilci kasar a musabakar Alkur’ani Mai Tsarki na duniya da su zama wakilai na gari.

Shugaban najeriya Muhammadu Buhari ya bukaci wadanda za su wakilci kasar a musabakar Alkur’ani Mai Tsarki na duniya, wanda za a yi a kasar Saudiyya a cikin wannan shekarar, da su nuna abin koyi. Shugaba Buhari ya mika wannan bukatar ce a sakonsa na rufe taron musabakar Alkur’ani na kasa da aka gudanar a garin Gombe a jiya Lahadi.

Da yake gabatar da jawabin shugaba Muhammadu Buhari, ministan muhalli a Najeriya Sulaiman Hassan Zarma ya fara ne da mika godiya wa ALLAH subuhanahu wata’ala, sannan yace a yayin da nake mika sakon taya murna ga dukkan wadanda suka fafata a musabakar, ina kira gare ku da ku tabbatar kun yi koyi da koyarwan addinin musulunci na hadin kai a tsakanin dukkan 'yan adam da kuma kyakkyawan dabi’a.

A nasa jawabin shugaban jami’ar Usman Dan fodiyo da ke Sakkwato farfesa Abdullahi Abdul Zuru ya yi bayanin makasudin shirya musabakar, da cewa hanya ce ta kulla abota a tsakanin 'yan kasa.

Ga dai wakilinmu a shiyyar Bauci Abdulwahab Muhammad da cikakken rahoton:

Your browser doesn’t support HTML5

Kiran Da Shugaba Muhammadu Buhari Yayiwa Dalibai Masu Musabaka 3'47"