Boko Haram: Mutanen Kumshe Sun Sha Azaba A Hannun Boko Haram

Your browser doesn’t support HTML5

Wani dan gudun hijira daga garin Kumshe da ya ga hotunan gine-ginen da aka ciro daga bidiyon kashe-kashe na 'yan Boko Haram, ya tabbatar da cewa lallai a garinsu aka aikata wannan abu. Duk da cewa bai ga hotunan kashe-kashen da aka yi ba, kuma bai ga hotunan 'yan Boko Haram rike da makamai ba, ya tuno da abubuwan da suka faru, da yadda Allah Ya kubutar da shi.