Daraktan gudanarwa na kamfanin NNPC, Mele Kyari ne ya sanar da rasuwar tasa a shafin sa na Twitter da safiyar yau sai dai bai bayyana sanadin mutuwar tasa ba.
We lost our esteemed Dr Muhammad Sanusi Barkindo. He died at about 11pm yesterday 5th July 2022. Certainly a great loss to his immediate family, the NNPC, our country Nigeria, the OPEC and the global energy community. Burial arrangements will be announced shortly.
— Mele Kyari (@MKKyari) July 6, 2022
Sanarwar tace: “Mun yi rashin mai girma Dakta Muhammad Sanusi Barkindo. Ya rasu ne da misalin karfe 11 na daren jiya 5 ga watan Yuli, 2022 . Babu shakka wannna babban rashi ne ga danginsa, da kamfanin NNPC, da kasarmu Najeriya, da kungiyar OPEC, da kuma kungiyar makamashi ta duniya. Za a sanar da sanar da shirye-shiryen jana’izar shi nan ba da dadewa ba.”
Dr Barkindo ya rasu yana da shekaru , 63 a duniya.
An nada Dr Barkindo a matsayin Sakatare Janar na OPEC a shekarar 2016 ya kasance dan Najeriya na hudu da ya rike wannan mukamin kuma mutum na 28 da ya rike matsayin.
Kafin zaben shi a matsayin Sakare Janar na OPEC, ya yi aiki a matsayin babban darektan kamfanin NNPC (GMD) tsakanin 2009 zuwa 2010.
Bayanai na nuni da cewa, jiya Talata marigayin ya yi wata ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari inda ya bayyana cewa wa’adinsa na shekaru shida a matsayin magatakardan kungiyar ta OPEC ya zo karshe.
Baya ga ziyarar Aso Rock, Dr Barkindo ya kuma gabatar da jawabi ranar a taron mai da iskar gas na Najeriya da aka gudana a Abuja.
Barkindo ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta hadin gwiwa tsakanin OPEC da kasashen da ba na OPEC ba kan daidaita kasuwannin mai, biyo bayan faduwar farashin mai a shekarar 2020.
A cikin wata sanarwa da kungiyar ta OPEC ta fitar, ta bayyana rasuwarsa a matsayin babban rashi ga daukacin iyalan kungiyar ta OPEC, masana'antar mai, da sauran kasashen duniya.
Jim kadan bayan wallafa sanarwar rasuwar sa mutane su ka fara aika sakon ta'aziya:
This is a big shock. Oh no so he didn’t even enjoy his retirement after all these yrs of work. Almighty God accept his soul and comfort his family. Sad
— george nwonye (@gnwonye) July 6, 2022
Didn%27t this same man visited Buhari yesterday at Aso Rock, where he notified the latter of the impending end to his tenure as the OPEC leader? Pls, what happened to him? 😪 May God forgive his shortcomings and grant him eternal rest.
— OBJ nt Obj (@jtuns) July 6, 2022
Your browser doesn’t support HTML5