Ba Zan Lamunci Cin Hanci Da Rashawa Ba – Babbar Mai Shari’a A Najeriya, Kudirat Kekereke-Ekun

Babbar Mai Shari'a a Najeriya, Kudirat Kekere-Ekun (Facebook/NTA)

Mai Shari'a Kudirat Kekereke-Ekun, ita ce mace ta biyu da ta taba rike wannan mukami a Najeriya baya ga Mai Shari’a Maryam Aloma Mukhtar.

Babbar Mai Shari’a a Najeriya (CJN) Kudirat Kekere-Ekun, ta ce ba za ta lamunci cin hanci da rashawa ba a karkashin shugabancinta.

Kekere-Ekun ta bayyana hakan ne a ranar Laraba bayan da majalisar dattawa ta tabbatar da ita a matsayin sabuwar Babbar Mai Shari’a a kasar.

Hakan na nufin ita ce mace ta biyu da ta taba rike wannan mukami a Najeriya.

“Dukkan kararrakin da aka shigar wadanda suka shafi batutuwan da suka faru gabanin zabe, za a kammalu su a kotun daukaka kara.” Kekereke-Ekun ta ce.

‘Yan majalisar Dattawan sun kwashe sa’o’i suna ta mata tambayoyin kan shirinta na samar da sauye-sauye a fannin shari’ar kasar.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne ya aika wa majalisar dattawa bukatar a tantance Kekereke-Ekun.

A watan Agusta Tinubu ya ba ta rikon kwarya sakamakon ritayar Mai Shari’a Olukayode Ariwoola da ya gabace ta.