Arewacin Najeriya Na Cikin Duhu Sakamakon Rugujewar Tashar Wutar Lantarki

Wutar lantarki ta katse a duk fadin kasar Najeriya

Kamfanin samar da wutar lantarki na Najeriya (TCN) ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa wata matsala da ta samu a tashoshin samar da wutar lantarkin na Kainji/Jebba ne ya haddasa katsewar.

A ranar 22 ga Oktoba, 2024, biyo bayan wata babbar matsala da aka samu a tashar wutar lantarki a kasar, yankin arewa ya tsinci kansa da katsewar wutar da ta shafi jihohi da dama a yankin.

Kamfanin samar da wutar lantarki na Najeriya (TCN) ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa wata matsala da ta samu a tashoshin samar da wutar lantarkin na Kainji/Jebba ne ya haddasa katsewar.

Hakan ya sa miliyoyin mazauna manyan garuruwa kamar Kano, Kaduna, da Sokoto suka rasa wutar lantarki.

A cewar TCN, injiniyoyi suna aiki tukuru don dawo da wutar lantarki, amma ba a bayar da takamaiman lokacin da za a shawo kan matsalar ba.

Wannan lamari dai ya sake zama wani kalubale a kasar da aka dade ana fama da rashin daidaiton samar da wutar lantarki, wanda ya sha yin tasiri a sassan gidaje da masana'antu.

Ko da yake ana kokarin inganta hanyoyin samar da makamashi a Najeriya, rugujewar wutar lantarki da ake yi akai-akai na ci gaba da kawo cikas ga ci gaba.

Hukumomin sun bukaci kwantar da hankula da hakuri yayin da suke aiki don shawo kan lamarin, yayin da kamfanonin rarraba wutar ke ci gaba da wayar da kai da fadakarwa a kafafen sadarwa na zamani da gidajen rediyo da talabijin.

~Yusuf Aminu Yusuf