An Yi Zaman Tattauna Makomar 'Yan Boko Haram Da Ke Mika Wuya a Jihar Borno

Your browser doesn’t support HTML5

Yayin da mayakan Boko Haram ke ci gaba da mika wuya, an yi zaman tattauna yadda za a samarwa mayakan makoma bayan da suka ajiye makamansu a jihar Borno.
A jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya, yayin da ake ci gaba da samun mayakan Boko Haram da ke mika wuya, hukumomi a jihar, tushen kungiyar ta Boko Haram, sun yi wani taro da masu ruwa da tsaki a jihar da nufin tattauna makomarsu. Ga rahoton Hussaina Mohammed daga Maiduguri.